Isa ga babban shafi

Jam'iyyar Narendra Modi ta rasa kujerar jihar Karnataka

Sakamako daga hukumar zaben kasar Indiya na tabbatar da cewa jam'iyya mai mulki ta Firaminista Narendra Modi ta rasa kujerar ta a babbar jihar Karnataka ta kudancin kasar shekara guda kafin zaben kasa.

Wasu daga cikin magoya bayan Firaministan Indiya Narendra Modi
Wasu daga cikin magoya bayan Firaministan Indiya Narendra Modi AP - Anupam Nath
Talla

Cikin farin ciki,an bayyana nasarar  jam'iyyar adawa ta Congress Party,wanda hakan ke dada nuni cewa yan adawa na kokarin dawowa da karfi a siyasar Indiya duk da cewa ta na rike da wasu kejeru daban da sakamakon na yau.

Firaministan kasar Indiya Narendra Modi
Firaministan kasar Indiya Narendra Modi AP - Manish Swarup

Bharatiya Janata (BJP, mai kishin addinin Hindu) jam’iyyar Firaminista  Modi ke rike da madafun iko na wannan yanki.

Jihar Karnataka tana da yawan jama'a sama da miliyan 60, kusan girman Biritaniya kuma babban birninta Bengaluru shine cibiyar fasahar Indiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.