Isa ga babban shafi
Najeriya

An tabbatar da zaben sabon Sarkin Kano malam Sanusi Lamido Sanusi

A Najeriya Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da mika sarautar Kano ga sabon Sarkin da aka zaba bayan rasuwar marigayi Mai martaba Alhaji Dr. Ado Bayero a karshen Mako.To ko wanene sabon Sarkin Kanon, ga dai dan takaitaccen Tarihinsa. 

Sarkin Kano Sanusi Lamido Sanusi
Sarkin Kano Sanusi Lamido Sanusi RFI Hausa
Talla

TARIHIN SABON SARKIN KANO

Tarihi dai ya nuna cewar a shekaarra 1961 ne aka haifi sabon Sarkin Kano Malam Sanusi Lamido Sanusi a ranar 31 ga watan Yuli.

Wannan dai ya nuna cewar sabon sarkin na da shekaru 2 ne kacal aka nada wanda ya gada wato marigayi Dr Ado Bayero a shekarar 1963.

A bangaren karatu kuwa sabon Sarki Malam Sanusi Lamido sanusi ya yi Digirin farko ne a Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya a fanning tsimi da tanadi, sai kuma wani digirin a jami’ar Khartoum ta kasar Sudan.

Sabon Sarkin ya dan yi koyarwa kadan a Jami’ar Ahmadu Bello kamin daga bisani ya koma aikin Banki a 1985 a Icon Limited da kuma Bankunan UBA da First Bank.

A nan ne fa Sanusi Lamido Sanusi ya kara samun ci gaba zuwa Gwamnan babban Bankin Najeriya a 2009.

Shi ne ya bankado badakalar wwaure kudi a baitul malin Najeriya abinda ya haifar da matsala tsakaninsa da hukumomin kasra ta Najeriya suka kuma saukar da shi daga kan jagorancin babban Bankin kasar a ran 20 ga Fabrarirun 2014, yanzu kuma shi ne sabon Sarkin Kano.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.