Najeriya
Za a ci gaba da shari'ar Saraki a watan Maris
Kotun ladabtar da ma’aikata ta Najeriya ta fitar da wata sanarwa, inda ta ce za ta ci gaba da shari’ar da ta ke yi wa shugaban majalisar dattawan kasar, Bukola Saraki a ranar 10 ga watan Maris mai zuwa.
Wallafawa ranar:
Talla
Mai Magana ya yawun kotun, Ibrahim Alhassan ya ce, kotun ta sanar da bangarorin da shari’ar ta shafa.
Ofishin Atone-Janar na kasar ne ya maka Saraki kotun akan tuhume tuhume guda 13 da ake yi masa da ya hada da bayar da bayanan karya dangane da kadarorin da ya mallaka a lokacin da ya ke gwamnan jihar Kwara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu