Isa ga babban shafi
Najeriya

Gwamnatin Najeriya za ta fara ciyar da dalibai

Gwamnatin tarayyar Najeriya za ta fara aiwatar da shirinta na ciyar da daliban makarantun Firamare kimanin miliyan biyar da dubu 500 da ke fadin kasar nan da watan Satumba mai zuwa.

Gwamnatin Najeriya za ta fara aiwatar da shirinta na bai wa daliban makarantun kasar abinci kyauta
Gwamnatin Najeriya za ta fara aiwatar da shirinta na bai wa daliban makarantun kasar abinci kyauta William Vest-Lillesoe/IBIS
Talla

Shugabar shirin ta kasa ce, Abimbola Adesanmi ta sanar da haka a yayin taron masu ruwa da tsaki kan shirin ciyar da dalibai abinci kyauta a garin Abeokuta da ke jihar Ogun.

Mrs. Adesanmi ta ce, gwamnatin za ta fara bayar da abinicin ne ga daliban aji 1 zuwa 3 kafin daga bisani ta fara bai wa daliban azuzuwan gaba, idan tattalin arzikin kasar ya inganta.

A jihar Ogun kadai, akwai kimanin dalibai dubu 200 da ke matakin aji daya zuwa 3 a makarantun gwamnati dubu 1 da 154  kamar yadda gwamnan jihar Ibikulne Amosun ya bayyana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.