Najeriya
Malaman makarantu na mutuwa a Jihar Lagos
Gwamnatin Jihar Lagos dake kudancin Najeriya tace malaman makarantun Sakandare 10 ke mutuwa a Jihar kowanne wata, sakamakon rashin lafiya da kuma yadda wasu kan yanke jiki su fadi.
Wallafawa ranar:
Talla
Babar Sakatariyar kula da malaman Jihar da kuma ofishin Fansho Sewanu Ayodele-Amosu ta bayyana haka a wani taro da aka gudanar a Jihar dan fadakar da malaman kan yada zasu kula da lafiyar su.
Mataimakiyar Gwamnan Jihar Idiat Adebule tace gwamnati zata ci gaba da sauke nauyin dake kan ta wajen kula da malaman.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu