'Yan Shi'a sun mutu a wasu Jihohin Najeriya ranar Ashura
Rahotanni sun ce an yi arangama tsakanin jami’an tsaro da mabiya mazhabar Shi’a a sassa da dama na Najeriya a daidai lokacin da ‘yan Shi’ar ke juyayin zagayowar ranar Ashura.
Wallafawa ranar:
A Funtua da ke jihar Katsina an kashe ‘yan Shi’a akalla 3 da dan sanda guda, yayin da a biranen Kano da Jos da Sokoto da kuma Kaduna, wasu da aka ce fararen hula ne suka afkawa ‘yan Shi’ar tare da kona wurarensu na ibada da asaran rayuka.
Sai dai wasu rahotanni da ba a tabbatar ba, sun ce ‘yan shi’ar 9 aka kashe a Katsina.
Da fari dai gwamnatin Jihohin da suka hada da Kaduna da Kano da Katsina da Kebbi sun haramtawa 'yan shi'a yin tattaki a wannan shekarar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu