Isa ga babban shafi
Najeriya

Masu garkuwa da Jamusawa biyu a Najeriya na bukatar Naira miliyan 60

Mutanen da suka yi garkuwa da wasu Jamusawa biyu a jihar Kaduna dake Najeriya sun gindaya sharudda kafin su sako Jamusawan da aka sace tun ranar Laraba data gabata.

Sifeto Janar na rundunar 'yan sandan Najeriya Ibrahim Idris
Sifeto Janar na rundunar 'yan sandan Najeriya Ibrahim Idris THISDAYLIVE
Talla

Jamusawan biyu sun hada da Peter Breunig da Johannes Buringer wadanda aka sace a kauyen Jenjela dake karamar Hukumar Kagarko na jihar Kaduna inda suka tafi wajen aikin hakar ma’adinai.

Majiyoyin samun labarai na cewa masu garkuwa da su na bukatar kudi Naira miliyan 60 kafin su sako Jamusawan.

Ganau sun bayyana cewa sai da masu satan Jamusawan suka kashe wasu ‘yan kauyen biyu kafin su yi awon gaba da Jamusawan.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.