Isa ga babban shafi
Najeriya

An saki daliban da aka yi garkuwa da su a Legas

An saki dalibai 6 na wata makaranta da ke jihar Legas a kudancin Najeriya bayan sun shafe sama da watanni biyu a hannun mutanen da suka yi garkuwa da su don karbar kudin fansa.

Daliban da aka wasu 'yan bindida suka yi garkuwa da su a jihar Legas ta Najeriya
Daliban da aka wasu 'yan bindida suka yi garkuwa da su a jihar Legas ta Najeriya punchng.com
Talla

Rahotanni sun ce, an saki daliban ne na makarantar Igbonla Model College bayan an sake biyan masu garkuwa da su Naira miliyan biyar a matsayin kudin fansa.

Wata majiyar tsaro ta ce, jumullar Naira miliyan 37 aka biya don ‘yanto daliban daga hannun mutanen.

A ranar 25 ga watan Mayun da ya gabata ne, wasu ‘yan bindiga sanye da kakin soji suka dirar wa makarantar, in da suka sace daliban daga dakin kwanansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.