Isa ga babban shafi
Najeriya

An umarci gwamnatin Lagos ta biya mutane diyya

Wata kotu a Najeriya ta umurcin gwamnatin jihar Lagos da ta dakatar da aikin rusa gidajen jama’ar da ke rayuwa a gabar ruwan teku, aikin da gwamnatin ta ce tana yin sa ne domin rage yawan masu aikata laifufuka.

Mazauna Otodo Gbame, Lagos na murna da hukuncin kotu
Mazauna Otodo Gbame, Lagos na murna da hukuncin kotu REUTERS
Talla

A cikin watan Oktoban da ya gabata ne mazauna unguwannin da lamarin ya shafa suka shigar da kara a gaban kotun, bayan da mahukunta suka fara rusa gidajensu, inda hukuncin kotun ya bukaci gwamnati ta shiga tattaunawa da jama’a kan yadda za a biya su kudaden diyya ko kuma inda za su a gaba.

Khadija Yusuf wata da ke rayuwa a irin wadannan unguwanni, ta ce sun yi farin ciki da hukuncin na kotun.

Khadija ta ce rusa matsuguninsu da suke rayuwa a Lagosn ya tursasawa mutane da dama barin garin duk da sun shafe shekaru suna rayuwa domin samun na abinci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.