Biri Ya Hadiye Miliyoyin Kudaden 'Yan Malisar Dattijan Najeriya
A Najeriya daya daga cikin yan majalisar dattawan kasar daga jihar Kaduna sanata Shehu Sani, ya bayyana dalilan da suka sanya cire sanata Abdullahi Adamu daga mukamin shugaban kungiyar sanatocin yankin arewacin kasar.
Wallafawa ranar:
Daga cikin dalilan inji shehu sani shine yadda wasu birrai suka sace naira miliyan 70 mallakar kungiyar bayan da daya ajiye su a gonar sa.
Acewar shehu Sani wannan na daga dalilan amma sauran abokan aikin su sun gaza bayyanawa.
Mataimakin shugaban majalisar Ike Ekweremadu ne ya sanar da matakin a zaman majalisar na yau.
A 'yan kwanakin nan dai ana ta samun rahotannin batan makudan kudade a Najeriyar ta hanyar cewa dabbobi ne ke cinye wa.
A makon jiya wata jamia a Hukumar Jarabawar shiga Jami'a ta sanar da cewa maciji ya hadiye miliyoyin kudaden Hukumar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu