Isa ga babban shafi
Najeriya-Ta'addanci

Dakarun hadaka sun kashe 'yan ta'adda 22 a yankin tafkin Chadi

Dakarun hadaka ta kasa da kasa sun kashe kimanin mayakan Boko Haram da a kungiyar ISWAP 22  a yayin wani samame da suka kai yankin tafkin Chadi.

Jami'an tsaron Najeriya a yankin arewa maso gabashin Najeriya
Jami'an tsaron Najeriya a yankin arewa maso gabashin Najeriya Getty Images
Talla

Babban jami’in yada labaran rundunar hadakar a N’Djamena, Laftanar Kanar Kamaruddeen Adegoke ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.

Kanar Adegoke ya ce an kashe ‘yan ta’addan ne a yankin karamar hukumar Abadam ta jihar Borno a ranar 27 ga watan Afrilu.

Ya ce  bayan gumurzu da suka yi tare da goyon bayan rundunar sojin sama ta musamman, nazarin da suka yi ya nuna cewa an kashe sama da ‘yan ta’adda 20, aka kuma kwace bindigogi kirar AK 47 da sauran manyan makaman yaki da suka hada da motoci masu sulke.

Adegoke  ya yi bayanin cewa dakarun sojin hadakan za su ci gaba da farautar ‘yan ta’adda a wani yunkuri na kara musu matsin lamba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.