Abba ya yi mamakin rashin bayyanar Ganduje a wajen bikin rantsuwa
A jawabinsa gaban taron rantsar da shi yau litinin, sabon gwamnan Kano Injiniya Abba kabir Yusuf ya diga ayar tambaya game da dalilin da ya hana tsohon gwamnan Jihar Abdullahi Umar Ganduje halartar wajen bikin mika mulkin ga sabuwar Gwamnati.
Wallafawa ranar:
Sabon Gwamnan na Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf lokacin da ya ke jawabi a filin wasa na Sani Abacha a Kano, inda ake ci gaba da bikin rantsuwar kama aikin sabuwar gwamnatin, ya yi shaguben cewa ko tsohon gwamnan na Kano na tsoron halartar wajen ne.
A cewar Abba Kabir ya gaji bashin fiye da Naira biliyan 200 daga gwamnatin Ganduje, inda ya ce gwamnatin sa za ta bi diddigin yadda aka kashe wadannan kudade.
Tsohon sakataren gwamnatin Kano Usman Alhaji ne ya mika mulkin a madadin tsohuwar gwamnatin ta Ganduje.
Zuwa yanzu dai ana ci gaba da shagulgulan murnar mika mulkin ga Abba Kabir Yusuf wanda ya yi nasarar lashe zaben watan Fabarairu da gagarumin rinjaye.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu