Isa ga babban shafi

Nnamdi Kanu ya umurci mukarabansa su kawo karshen rikici

Jagoran masu fafutukar kafa kasar Biafra a Najeriya Nnamdi Kanu, ya umarci daya daga cikin mukarabansa Simon Ekpa da ya kawo karshen tayar da kayar baya a yankin kudu maso gabashin kasar. 

Wasu 'yan kungiyar IPOB masu fafutukar kafa kasar Biafra.
Wasu 'yan kungiyar IPOB masu fafutukar kafa kasar Biafra. http://naijagists.com
Talla

Ekpa na daya daga cikin kwamandojin Kanu kuma shi ne ya yi ikirarin cewa ya karbi ragamar shugabancin kungiyar ta IPOB bayan tsare Kanun.  

Magoya bayan Nnamdi Kanu
Magoya bayan Nnamdi Kanu AFP PHOTO / PIUS UTOMI EKPEI

Jagoran kungiyar ta IPOB da ke tsare yanzu haka, a cikin wasikar da ya rubuta da hannu zuwa ga Simon Ekpa, ya bukace shi  da ya yi sanarwar amincewa da karbar umarni daga gare shi. 

Nnamdi Kanu Shugaban kungiyar IPOB a  Najeriya
Nnamdi Kanu Shugaban kungiyar IPOB a Najeriya REUTERS/Afolabi Sotunde/Files

Aloy Ejimakor, lauya na musamman dake kare Nnamdi Kanu, ya wallafa labarin wasikar da shugaban kungiyar ta IPOB ya rubuta da hannu a shafin sa na Twitter da aka tabbatar a jiya Juma’a. lauyan, a wata sanarwa da ya fitar dauke da wasikar, ya ce Nnamdi Kanu ya rubuta wasikar ne a ranar 24 ga watan yuli lokacin da daya daga cikin mukarabansa a yunkunri na kafa kasar Biafra, Simon Ekpa ya ziyarce shi a ofishin hukumar tsaro ta farin kaya (SSS). 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.