Isa ga babban shafi
Nijar

An nada sabon Firaminista a jamhuriyar Nijar

Sabon Shugaban kasar Jamhuriyar Nijar Bazoum Mohammed ya nada Ouhoumadou Mahamadou a matsayin Firaministan da zai jagoranci gwamnatin kasar.

Sabon shugaban Jamhuriya Nijar lokacin rantsar da shi a ranar 2 ga watan Afrelun wannan shekara 2021
Sabon shugaban Jamhuriya Nijar lokacin rantsar da shi a ranar 2 ga watan Afrelun wannan shekara 2021 © Compte officiel du Président de la République du Niger - Twitter
Talla

Sanarwar da fadar shugaban kasa ta gabatar tace sabon shugaban ya sanya hannu kan dokar nada tsohon Babban Hafsa a fadar shugaban kasa a matsayin Firaministan wanda zai kafa gwamnati nan bada dadewa ba.

Sabon Franmninstan jamhuriyar Nijar Ouhomou Mahamadou da zai jagoranci kafa sabuwar gwamnatin kasar, sabon shugaban kasar Bazoum Mohamed ya nada shi ranar 4 ga watan Afrelun shekarar 2021.
Sabon Franmninstan jamhuriyar Nijar Ouhomou Mahamadou da zai jagoranci kafa sabuwar gwamnatin kasar, sabon shugaban kasar Bazoum Mohamed ya nada shi ranar 4 ga watan Afrelun shekarar 2021. © ©Presidence de la republique du Niger

Sabon Firaministan ya lashe zaben Majalisar dokoki a bara kuma ya taba rike mukamin ministan makamashi da ma’adinai da masana’antu tsakanin shekarar 1991 zuwa 1993, yayin da yayi ministan kudi tsakanin shekarar 2011 zuwa 2012.

Firaministan na daga cikin makusantar tsohon shugaban kasa Mahamadou Issofou kuma yana da karfin fada aji a Jam’iyar PNDS Tarayya mai mulkin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.