Harin kwanton bauna ya halaka sojojin Nijar biyar
Akalla sojojin Nijar 5 sun mutu ya yin da wasu 4 suka samu raunuka a wani harin da 'yan bindiga dauke da makamai suka kai wa ayarin motocin su ranar Lahadi, kan hanyar Tabaraga-Arlit kusan kilomita 300 daga Aagadas.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kunna - 01:28
Jamhuriyar Nijar dai na daga cikin kasashen yankin Sahel, da ke fama da hare-haren masu tayar da kayar baya da suka addabi kasar.
Tuni akayi jana'izar sojojin da suka mutu yau da safe bisa jagorancin shugaban hafsan sojojin kasar a garin Arlit.
Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken rahoton da oumarou Sani ya hada daga Nijar din.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu