Ƙungiyar tsagerun Neja-Delta ta yi barazanar fara kai hare-hare bututun mai
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:45
Ƙungiyar tsageru ta yankin Neja-Delta a kudancin Najeriya mai suna Niger Delta Avengers ta yi barazanar durkusar da tattalin arzikin Najeriya ta hanyar ci gaba da kai hare-hare a kan matatun man fetur na ƙasar da kuma 'yan siyasar yankin da ke "haɗa kai da gwamnati" saboda da abin da ta kira rashin cika mata alkawura.
Kungiyar ta yi zargin cewar duk da gudumawar da yankin su ke bayarwa ya kasance koma baya wajen ci gaba, yayin da ake watsi da bukatun su.
Dangane da wannan batu ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki Dr Isa Abdullahi na Jami’ar Kashere, kuma kuna iya latsa alamar sauti domin sauraron yadda zantawar su ta gudana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu