Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Barista Abdullahi Jalo kan halin da ake ciki a jihar Gombe
Wallafawa ranar:
Rahotanni daga Jihar Gombe a Najeriya sun ce ana ci gaba da zaman dar-dar sakamakan matsalar da aka samu a makon jiya, lokacin da wasu 'yan bangar siyasa suka tare tsohon gwamnan jihar Sanata Danjuma Goje, lokacin da ya ke kokarin shiga garin. Bayan sun ce an samu arangama tsakanin masu goyan bayan tsohon gwamnan da kuma gwamna Inuwa Yahya mai ci. Dangane da wannan matsala, mun tuntubi Barr Abdullahi Jalo, daya daga cikin dattawan jihar kuma ga tsokacin da yayi akai.