Dandalin Nishadi
Hukumar Hisba ta kama fitacciyar ‘yar tiktok kuma jarumar fina-finai Murja Kunya
Wallafawa ranar:
Kunna - 17:30
A cikin shirin na wannan mako muna tafe da dambarwar da ta dabaibaye kamun da hukumar Hisba a jihar Kano da ke arewacin Najeriya ta yiwa fitacciyar ‘yar tiktok kuma jarumar fina-finai Murja Kunya.Akwai mu dauke da tattaunawa tare da mawaki Abdallah Abdallah Muhammad da aka fi sani da Amdaz ko kuma Excellency.Sannan zamu kawo muku fashin baki kan rikicin da ya kunno kai tsakanin fitattun mawakan gambarar Najeriya wato Edris Abdulkareem da kuma Burna Boy.