Najeriya: Wa'adin karbo kudin gwamnati daga hannun manoma ya cika
Wallafawa ranar:
Kunna - 14:19
Shirin 'Ra'ayoyin Masu Sauraro' na wannan rana ya baku damar tattaunawa ne akan cikar wa’adin da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya baiwa jami’an tsaro domin kwato sama da naira biliyan 500 daga cikin kudaden rancen da aka bai wa manoma a karkashin babban bankin Najeriya na ‘Anchor borrower’ ke cika.
Alkalluman da bankin Najeriya CBN ya fitar sun nuna cewar zuwa shekarar 2022, manoma akalla miliyan 4 da dubu 800 ne suka samu tallafin shirin bunkasa noman na ‘Anchor Borrower’, sai dai wani rahoton asusun ba da lamuni na duniya IMF ya nuna cewar, kashi 76 cikin 100 na adadin kudaden rancen da bankin na CBN ya bai wa monama a Najeriyar ne ba a maida ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu