Isa ga babban shafi
Syria

An dage taron sasanta rikicin Syria

Jakadan Majalisar Dinkin Duniya kan sasanta rikicin kasar Syria Staffan de Mistura ya ce an dage taron da aka shirya yi ranar 8 ga wannan watan na Fabairu zuwa ranar 20 don bai wa bangaren 'yan adawa damar sasanta tsakaninsu.

Shekaru fiye da biyar da barkewar yaki a Syria, mutane sama da 300,000 sun mutu
Shekaru fiye da biyar da barkewar yaki a Syria, mutane sama da 300,000 sun mutu
Talla

Jami’in wanda ke yi wa Majalisar Dinkin Duniya bayani ya ce an dauki matakin ne dan bai wa bangarorin ‘yan adawan kasar damar shiryawa a tsakanin su.

Kasashen Rasha da Turkiya da Iran sun jagoranci wani taro a makon jiya a birnin Astana da ke kasar Kazakhstan dan ganin an samo hanyar kawo karshen rikicin da ya lakume rayukan mutane sama da 310,000 yanzu haka.

Shekaru fiye da biyar kenan ake yaki a Syria, yakin da ya ki ci ya ki cinyewa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.