Isa ga babban shafi
Kwallon kafa

Faransa ta fara gasar cin kofin duniya da kafar dama

Kasar Faransa ta lallasa takwararta Hounduras da ci 3-0 bayan da suka kara a wasansu na farko a gasar cin kofin duniya da ake yi a kasar Brazil.

Karim Benzema na kasar Faransa
Karim Benzema na kasar Faransa REUTERS/Murad Sezer
Talla

Dan wasan Faransa Karim Benzema ne ya zira kwallaye biyu daga cikin kwallaye uku, wanda hakan ya sa yana da kwallaye 23 ke nan da ya zirawa kasarsa.

Masu sharhi kan kwallon kafa na bayyana cewa haskarwar da Benzema ya yin a da nasaba da rashin zuwan Frank Ribery gasar.

Benzema ya zira kwallo ta farko wacce aka yi amfani da fasahar tantance sigar kwallo raga kamin a fayyace sahihancin kwallon a karon farko a gasar kasa da kasa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.