Ronaldo ya fice daga dakin taro
Gwarzon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Madrid, Christiano Ronaldo ya fice daga dakin taron manema labarai da aka gudanar a jiya Talata bayan an tambaye shi a game da kwallayen da ya zura a wasannin da kungirsa ta yi a waje a cikin wannan kakar.
Wallafawa ranar:
Ronaldo dai mai shekara 31 da haihuwa ya zura kwallaye 32 cikin wannan kakar amma tun a ranar 29 ga watan Nuwamban bara raban da ya ci kwallo a waje .
A martanin da ya mayar, dan wasan ya ce, wanene ya ci yawan kwallaye fiye da shi a waje tun lokacin da ya koma kasar Spain da taka leda.
Ronaldo dai shi ya fi yawan kwallaye a gasar cin kofin zakarun Turai, inda ya zura kwallaye 88 a cikin wasanni 121.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu