Isa ga babban shafi
Wasanni

An karrama 'yan wasan Albania

Al’ummar kasar Albania sun karrama ‘yan wasan tawagar kwallon kafa ta kasar duk da cewa an fitar da su daga gasar cin kofin kasashen Turai da ake gudanarwa a Faransa.

Tawagar kwallon kafa ta Albania a yayin buga gasar ta Euro 2016 a Faransa
Tawagar kwallon kafa ta Albania a yayin buga gasar ta Euro 2016 a Faransa AFP PHOTO / KAREN MINASYAN
Talla

‘Yan wasan sun samu kyakkayawar tarba tamkar wadanda suka lashe kofin gasar bayan sun koma gida a jiya Alhamis.

A karon farko kenan a tarihi da kasar ta halarci irin wannan babbar gasar a duniya, kuma an bayyana ‘yan wasan a matsayin gwarzaye saboda nasarar da suka samu a kan Romania.

Gwamanatin kasar ta yi alkawarin bai wa ‘yan wasan Fasfo na Diflomasiya saboda abinda da suka yi na daga darajar kasar a idon duniya.

Sannan kuma gwamantin ta bai wa tawagar kwallon kafar karin kudi har Euro miliyan 1.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.