Wasanni
Falcao zai yi gwajin lafiyarsa
Dan wasan gaba na Colombia Radamel Falcao zai yi gwajin lafiyarsa don tantance shi ko ya na da kuzarin dawowa Monaco don ci gaba ta murza tamnaula.
Wallafawa ranar:
Talla
Falcao mai shekaru 30 bai buga gasar Ligue 1 ba tun lokacin da ya sha naushi a kai a wasan da suka doke Nice da ci 4-0 makwanni uku da suka gabata.
Matukar dai lilkitoci suka bayar da tabbacin cewa ya samu cikakkiyar lafiya, to lallai zai buga wasan da Monaco za ta yi da Toulouse a ranar Jumma’a mai zuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu