Ghana ta doke Uganda a gasar kofin Afrika
Kasar Ghana ta doke Uganda da ci daya mai ban haushi a fafatawar da suka yi a jiya a gasar cin kofin Afrika da ake gudanarwa a Gabon.
Wallafawa ranar:
Andre Ayew ne ya jefa kwallon a bugun daga kai sai mai tsaren gida kafin tafiya hutun rabin lokaci, abin da a yanzu ya bai wa Ghana damar samun maki uku a rukuninsu na D.
Ghana ta samu damar bugun fanariti ne bayan Isaac Isinde na Uganda ya yi wa Gyan Asamoah keta a cikin gidan mai tsaren ragar Uganda.
Yanzu haka Ghana ce ke jan raga a rukunin D sakamakon wannan nasara da ta samu.
Tun bayan fara gasar a ranar Asabar da ta gabata, kasashe uku ne kadai da suka hada da Ghana da Senegal da Jamhuriyar Demokradiyar Congo suka yi nasarar lashe wani wasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu