Isa ga babban shafi
Wasanni

Pillars da Rangers za su fafata wasan karshe na gasar kofin Aiteo

Kungiyoyin Enugu Rangers da Kano Pillars sun samu nasarar kaiwa zagayen karshe na gasar cin kofin kalubalen Najeriya wato Aiteo Cup.

Kofin gasar kalubale ta kungiyoyin Najeriya (Aiteo Cup)
Kofin gasar kalubale ta kungiyoyin Najeriya (Aiteo Cup) Photo credit: Aiteo cup
Talla

A ranar Laraba ne dukkanin kungiyoyin biyu, suka fafata wasannin kusa dana karshe, inda a filin wasa na Sani Abacha dake birnin Kano, Enugu Rangers suka samu nasara akan Nasarawa United da kwallaye 4-2.

Nasarawa United ce dai ta soma jefa kwallaye biyu a a wasan, kafin daga bisani Enugu Rangers sun rama, tare da kara kwallaye biyu.

Wasan tsakanin Kano Pillars da Katsina United kuwa ya gudana ne a birnin Legas, wanda aka tashi 2-2, hakan yasa aka kai ga bugun daga kai sai mai tsaron gida, inda Pillars ta samu nasara kan Katsina United da kwallaye 4-1.

A ranar 24 ga watan Oktoban da muke ciki, za’a buga wasan karshe na gasar cin kofin kalubalen na Aiteo a filin wasa na Stephen Keshi dake garin Asaba a jihar Delta.

Kungiyar da ta yi nasarar lashe kofin na Aiteo ce za ta wakilci Najeriya, a gasar cin kofin kalubale na zakarun kungiyoyin nahiyar Afrika a kaka mai zuwa, wato CAF Confederations Cup.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.