Isa ga babban shafi

Al Ahly ta lashe kofin zakarun nahiyar Afrika karo na 11

Kungiyar kwallon kafa ta Al Ahly a Masar ta lashe kofin zakarun nahiyar Afrika karo na 11 bayan doke Wydad Casablanca ta Morocco a birnin Cairo.

Tawagar Al Ahly bayan nasarar lashe kofin zakarun nahiyar Afrika karo na 11.
Tawagar Al Ahly bayan nasarar lashe kofin zakarun nahiyar Afrika karo na 11. REUTERS - ABDELHAK BALHAKI
Talla

Kwallon mai tsaron baya na Al Ahly Mohamed Abdelmonem ce ta taimakawa kungiyar samun kofin bayan da ta basu damar yin canjaras da kwallo 1 da 1 a haduwar ta jiya.

Tun farco Wydad ta fara zura kwallo ta hannun dan wasanta Yahia Attiyat amma kuma farkewar Abdelmonem ya baiwa Al Ahly nasara fa fifikon kwallayenta 2 na haduwarsu ta farko, inda a jumulla suka tashi wasa 3 da 2.

Cikin wannan kaka Ahly ta zura kwallaye 27 ciki har da 4 da Abdelmonem ya zura wanda suka bata damar kwace kambun na zakarun nahiyar Afrika daga hannun Wydad da ta lashe a bara.

Nasarar ta Al Ahly ta kawo karshen shan kayen da kungiyar ta yi har sau 2 a wasannin karshe hannun Wydad.

Sabanin Turai, karkashin gasar ta Afrika har yanzu kwallo a waje na da maki biyu ne yayinda ta gida ke da maki guda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.