Isa ga babban shafi
Gambia

Ana zaben 'Yan Majalisu a Gambia

Al’ummar Gambia na gudanar da zaben ‘yan majalisu a karon farko tun bayan kawar da gwamnatin Yahya Jammeh da ya shafe shekaru 22 kan karagar mulki. A lokacin mulkinsa, Jammeh kan yi biris da majalisar kasar, in da ya ke kafa dokokinsa ba tare da tuntubar su ba. 

Ana zaben 'Yan Majalisu a Gambia
Ana zaben 'Yan Majalisu a Gambia RFI/Claire Bargelès
Talla

Sama da mutane dubu 880 ke da damar kara kuri’a a zaben da aka soma tun da misalin karfe 8 na safe agogon GMT.

Zaben wani gwaji ne ga jami’iyyun adawa da dama da suka hada kai wajen kawar da gwamnati Jammeh a watan Disamba bara, kuma sabanin cikin gida da aka samu tsakanin wadannan jam’iyyu bayan rantsar da shugaba Adama Barrow ya nuna cewa kowa ta kansa ya ke a zaben na yau.

Jam’iyyu 9 ne ke takarar, ciki har da ta Jammeh da Jam’iyyar UDP da sarakuna ke da karfi a ciki.

Majalisar kasar na da kujeru 53, sai dai an samu karin 5 kan wanda ake da su a 2012.

Tsawon shekarun da Jammeh ya yi ya na tafiyar da kasar, babu batun bai wa ‘yan majalisu fifiko, sai dai a wannan lokaci Adama Barrow ya sauya wannan al’ada.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.