Harin bam ba zai hana mu yin zaben shugaban kasa ba - Zimbabwe
Gwamnatin Zimbabwe ta ce, harin bam din da aka kai kan taron yakin neman zaben jam’iyya mai mulki,, ta Zanu-PF da shugaban kasar Emmerson Mnangagwa ke jagoranta, ba zai sa a dage zaben shugabancin kasar da aka shirya za a yi, a ranar 30 ga watan Yuli mai zuwa ba.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kwana guda bayan kai harin da shugaba Mnangagwa ya ce shi aka son hallakawa, rundunar ‘yan sandan kasar ta ce mutane 49, suka jikkata a harin.
Daga cikin wadanda harin na birnin Bulawayo ya rutsa da su akwai mataimakan shugaban kasar guda biyu, wato, Kembo Mohadi da Constantino Chiwenga.
Zaben shugabancin kasar da za a yi nan da makwanni 5, shi ne na farko da zai gudana, tun bayan fara mulkin shugaba Robert Mugabe mai Murabus da ya shafe shekaru 37 yana jagorancin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu