Isa ga babban shafi
Liberiya

An kori wani jami’in zabe a Liberiya bayan yin coge

Hukumar gudanar zabe a Liberiya ta sallami Jami’in yada labaranta bayan yunkurin aikawa Jam’iyyar Adawa ta CDC ta sakon ita ke kan gaba a zaben shugaban kasa da aka gudanar a 11 ga watan Octoba.A sakon wasikar ta Bobby Livingstone, ya tsara cewa Shugaba Sirleaf ta Jam’iyyar UP ita ke da yawan kuri’u kashi 32.7 amma kuma jam’iyyar adawa ta CDC ke da rinjayen kuri’u tsakanin ta da ‘yan takara 16.Tun da farko Jam’iyyar adawa ta CDC ta yi zargin tabka magudi tare da neman bukatar an sallami shugaban hukumar gudanar da zaben.Wannan zargin kuma na CDC ya kara cusa shakku a cikin kasar da ke kokarin kammala zabe karo na biyu bayan kawo karshen yakin shekaru 14 da ya yi sanadiyar mutuwar mutane kimanin 250,000. 

Shugaban hukumar Zaben Liberia  James Fromayah, a lokacin da yake ganawa da manema Labarai
Shugaban hukumar Zaben Liberia James Fromayah, a lokacin da yake ganawa da manema Labarai REUTERS/Luc Gnago
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.