Obama ya gana da wasu shugabannin Afirka a fadarsa
Shugaban Amurka Barack Obama ya jinjinawa shugabannin kasashen Sierra Leone, Malawi, Senegal da kuma Cape-Verde wadanda ya bayyana su a matsayin wadanda suka samar da ci gaba ga dimokuradiyya a Afrika.
Wallafawa ranar:
Shugaba Obama ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da shugabannin a fadars White House a wani matakin na inganta hulda da samar da ci gaban kasashen Afrika.
Yanzu haka dai wadannan kasashe hudu, na tafiya ne a kan kyakkyawan tsari na dimokuradiyya, duk da cewa wasu daga cikinsu sun taba yin famada juyin mulki ko kuma ayyukan tawayen da ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane kamar dai Sierra Leone.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu