Isa ga babban shafi
Malawi

Na’urar Kidayar Kuri’un zaben Malawi ta lalace

Na’urar da ake kidayar Kuri’u a kasar Malawi ta samu matsala a lokacin da aka fara kidayar kuri’un zaben shugaban kasa da aka gudanar a cikin wannan makon. Jami’an hukumar zaben sun koma yin amfani da Fax da sakon email wajen tattara sakamakon zaben.

Shugabar kasar Malawi, Joyce Banda tana kada kuri'arta a zaben da ta ke neman wa'adi na biyu.
Shugabar kasar Malawi, Joyce Banda tana kada kuri'arta a zaben da ta ke neman wa'adi na biyu. REUTERS/Eldson Chagara
Talla

Hukumar zaben tace za’a samu tsaikun fitar da sakamakon zaben da aka gudanar a ranar Talata saboda matsalar.

Zuwa yanzu kuma babu wani sakamako da aka fitar inda Shugaba mai ci Joyce Banda ke takara da Peter Mutharika dan uwa ga tsohon shugaban kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.