Isa ga babban shafi
Nijar

Tsare minista saboda da zargin cinikin jarirai a Nijar

An cafke ministan noman Jamhuriyar Nijar Malam Abdou Labo, wato daya daga cikin manyan jami’an gwamnatin kasar da ake zargi da hannu a fataucin jarirai.

Mahamadou Issoufou shugaban Jamhuriyar Nijar.
Mahamadou Issoufou shugaban Jamhuriyar Nijar. Laura-Angela Bagnetto
Talla

Minista Abdou Labo na daya daga cikin daga cikin mutanen da ake zargin cewa sun yi cinikin jarirai daga wasu kasashe, da suka hada Najeriya, Benin da kuma Burkina Faso.

Kimanin wata daya da ya gabata ne wannan zance ya taso a kasar ta Nijar, kuma tuni aka cafke matan wasu manyan jami’ai na kasar da suka hada da matar Abdou Labo da kuma shugaban Majalisar Dokokin kasar Hama Amadou, wadanda aka ce sun sayo jarirai domin mayar da su a matsayin ‘yayansu daga wadancan kasashe.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.