Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

Kotu ta yi watsi da karar da Pistorius ya shigar

Kotu a kasar Afirka ta Kudu ta yi watsi da karar da Oscar Pistorius tsohon zakaran gudun nakasassu na dunya ya shigar, inda yake neman a sassauta hukuncin dauri da aka yanke masa bayan ya amince da cewa shi ne ya kashe masoyiyarsa Reeva Steenkamp.

Oscar Pistorius.
Oscar Pistorius. REUTERS/Mike Hutchings/Files
Talla

Wannan dai ita ce damar karshe da Pistorius ke da ita domin ganin cewa an soke hukuncin daurin da aka yanke masa.

Yanzu dai dan wasan zai fuskanci hukuncin akalla daurin shekaru 15 a gidan yari sakamakon kisan budurwar tasa a ranar 14 ga watan Fabairun shekarar 2013, wato a ranar masoya, ta hanyar harbin ta da bindiga amma ya ce, lamarin ya faru ne cikin  kuskure.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.