Isa ga babban shafi
South Africa

Kotu A Kasar Africa ta Kudu Za Ta Sake Duba Zargin Almundahana 800 Da Ake Yiwa Shugaba Jacob Zuma

Wata Kotu a kasar Africa ta Kudu ta ce Shugaban kasar Jacob Zuma zai fuskanci zargin laifukan cin hanci da rashawa 800 wadanda aka jingine tun shekara ta 2009.

Shugaba Jacob Zuma na Kasar Africa ta Kudu.
Shugaba Jacob Zuma na Kasar Africa ta Kudu. REUTERS/Mike Hutchings
Talla

Zargin wanda ya shafi miliyoyin kudade wajen sayen makamai, Mai shigar da kara ya jingine su ne domin baiwa shugaba Jacob Zuma damar tsayawa takarar shugabancin kasar a wancan lokaci.

Alkalin kotu dake Pretoria, Aubrey Ledwaba ya bayyana cewa sun jingine karar a wancan lokaci amma  yanzu ya dace a sake duba batun.

A cewar mai shigar da kara tilas aka jingine karar saboda katsalandan cikin shari'ar da wasu ‘yan siyasa ke yi, kamar yadda aka saurare su a zantuka ta wayoyin sadarwan su.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.