Najeriya zata kafa kotunan yaki da cin hanci da rashawa
Gwamnatin Najeriya tace ta kusa kammala shirin kafa kotuna na musamman da zasu dinga shari’ar zargin cin hanci da rashawa da kuma satar jama’a ana garkuwa da su dan karbar kudade.Farfesa Itse Sagay, shugaban kwamitin da shugaban kasar ya kafa dan bada shawara kan yadda za’a inganta aikin yaki da cin hanci da rashawa ya bayyana haka.
Wallafawa ranar:
Farfesa Sagay yace sun kusa kammala aikin su, wanda ake saran shugaba Muhamamdu Buhari zai gabatar ga Majalisa domin amincewa da dokar.
Bangaren shari’a na daga cikin manyan matsalolin da ake zargi da hana ruwa gudu wajen shari’ar wadanda ake zargi da satar kudaden talakawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu