Isa ga babban shafi
MDD-Liberia

Sojojin Liberia sun karbi ragamar tafiyar da tsaro

Sojojin kasar Liberia sun karbi ragamar samar da tsaro a kasar a karon farko tun bayan kawo karshen yakin basasa, shekaru 13 da suka gabata. Majalisar Dinkin Duniya na shirin janye dakarunta 4,000 da suka rage a kasar daga cikin 15,000 da aka girke na tsawon lokaci.

Sojojin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya zasu fice Liberia
Sojojin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya zasu fice Liberia REUTERS/James Giahyue
Talla

Za a bar kadan daga cikin dakarun Majalisar Dinkin Duniya wadanda zasu dinga taimakawa idan halin hakan ya yi.

A baya an rusa rundunar ‘Yan Sanda da sojin kasar saboda rawar da suka taka na goyan bayan bangarorin yakin basasar kasar, matsalar da ta jefa kasar cikin tashin hankali mai tsanani.

Sojojin gwamnati da ‘Yan tawaye sun yi wa mata fyade tare da kisan daruruwan mutane a rikicin kasar tsakanin 1989 zuwa 2003.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.