Isa ga babban shafi
Afrika ta kudu

Ana zaben kananan hukumomi a Afrika ta kudu

Alummar kasar Africa ta Kudu na gudanar da zabukan kananan Hukumomi a yau Laraba, a wani mataki da zai gwada karfin Jam’iyyar da ke mulki ta ANC.

Jam'iyyar ANC na tsaka mai wuya a zaben kananan hukumomi
Jam'iyyar ANC na tsaka mai wuya a zaben kananan hukumomi REUTERS
Talla

Ana ganin zaben tamkar zakaran gwaji daji ga gwamnatin Jacob Zuma da ke fuskantar suka a Afrika ta kudu kan zargin rashawa da tabarbarewar tattalin arziki.

Jam’iyyar ANC dai na iya shan kaye a zaben ko kuma rasa samun kuri’u a wasu mazabun, da watakila suka hada da manyan biranen kasar kamar Pretoria, da Johannesburg da birnin Port Elizabeth.

Ganin yadda tattalin arzikin kasar ke cikin wani hali da kuma rashin ayyukan yi ga matasaa, Jami’yyun adawa na ganin za su bada mamaki a zaben.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.