Isa ga babban shafi
Burudi

Manyan Jami'an Soja da na 'Yan Sanda na tserewa daga Burundi

A kasar Burundi, manyan sojoji da ‘yan sanda akalla 10 ne suka tsere suka bar kasar cikin wannan wata gudun kada a muzguna masu karkashin Gwamnatin Shugaba Pierre Nkurunziza.

Shugaban Burundi Pierre Nkurunziza
Shugaban Burundi Pierre Nkurunziza REUTERS/Evrard Ngendakumana
Talla

Wani masanin harkokin tsaron kasar Gratien Rukindikiza ya ce wadan da suka gudu sun  zarce 13,  kuma sun tsere ne sun bar kasar don fargaban abinda zai biyo baya saboda kabilar da suka fito ko kuma saboda ana zargin suna goyon bayan ‘yan adawa.

Kungiyoyin kare hakkin bil'adama na zargin Gwamnatin Shugaba Pierre Nkurunziza wanda ‘yan kabilar sa ta Hutu suka fi yawa a ciki, da muzgunawa sauran kabilu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.