Isa ga babban shafi
Congo

Mutane 14 sun rasa rayukansu a Congo

Akalla mutane 14 aka tabbatar da mutuwar su sakamakon wani hari da ake zargin tsoffin yan tawayen Congo Brazaville da kaiwa cikin wani jirgin kasa.

Wasu mutane mazauna birnin Brazaville da suka tsere daga gidajensu sakamakon barazanar tsaro
Wasu mutane mazauna birnin Brazaville da suka tsere daga gidajensu sakamakon barazanar tsaro
Talla

Kakakin 'yan sanda Jules Monkala Tchomou, yace cikin wadanda suka rasa rayukansu, a lokacin harin da ‘yan tawayen Ninja Nsilolulou suka kai, harda yara kanana da kuma sojoji guda biyu.

Ita dai kungiyar Ninja Nsiloulou ta gwabza yakin basasa sau biyu a kasar, kuma tana karkashin wani malamin addinin Krista ne da ake kira Frederic Bintsamou, wanda mabiyan sa ke kira manzo.

Tun a watan Aprilu wannan shekara rundunar sojin kasar ta Congo ta girke jami’anta a kudancin birinin Brazaville bayan harin da ‘yan a’addan suka kai inda suka kashe mutane 17.

A shekara ta 2003 jagoran ‘yan tawayen, Bitsango ya taba rattaba hannu kan yarjejeniyar sulhu da gwamnatin kasar.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.