Mutane 14 sun rasa rayukansu a Congo
Akalla mutane 14 aka tabbatar da mutuwar su sakamakon wani hari da ake zargin tsoffin yan tawayen Congo Brazaville da kaiwa cikin wani jirgin kasa.
Wallafawa ranar:
Kakakin 'yan sanda Jules Monkala Tchomou, yace cikin wadanda suka rasa rayukansu, a lokacin harin da ‘yan tawayen Ninja Nsilolulou suka kai, harda yara kanana da kuma sojoji guda biyu.
Ita dai kungiyar Ninja Nsiloulou ta gwabza yakin basasa sau biyu a kasar, kuma tana karkashin wani malamin addinin Krista ne da ake kira Frederic Bintsamou, wanda mabiyan sa ke kira manzo.
Tun a watan Aprilu wannan shekara rundunar sojin kasar ta Congo ta girke jami’anta a kudancin birinin Brazaville bayan harin da ‘yan a’addan suka kai inda suka kashe mutane 17.
A shekara ta 2003 jagoran ‘yan tawayen, Bitsango ya taba rattaba hannu kan yarjejeniyar sulhu da gwamnatin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu