Sama da mahaukata 100 sun tsere daga asibiti a Kenya
Rahotanni daga kasar Kenya, sun tabbatar da cewa sama da mahaukata 100 ne suka tsere daga asibitin masu tabin hankali da ke birnin Nairobi.
Wallafawa ranar:
Mahaukatan sun samu damar tserewar, bayanda likitoci da ma’aikatan jinyar asibitin masu tabin hankalin suka tsunduma cikin yajin aikin gama gari, da ma’aikatan lafiya suka fara a kasar, domin neman karin albashi.
Babban kwamandan rundunar ‘yan sandan birni Nairobi Japeth Koome, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa, tuni suka kaddamar da farautar, masu tabin hankalin da suka cika rigarsu da iska, sun kuma samu nasarar kama wasu daga cikinsu.
Sama da ma’aikatan lafiya da suka hadar da masu bada magani, likitoci, da kuma ma’aikatan jinya 5000 ne suka shiga yajin aikin, domin tilastawa gwamnatin Kenya yi musu karin kashi 300 bisa albashin da ake biyansu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu