Burundi ta soke kungiyar kare hakkin jama'a
Gwamnatin Burundi ta haramta wata kungiyar kare hakkin bil'adama da tafi dadewa tana aiki a kasar, da kuma ke ci gaba da fallasa irin munanan ayyukan da ake aikatawa.
Wallafawa ranar:
Wata sanarwar gwamnatin ta zargi kungiyar mai suna Iteka League da bata sunan gwamnati da cusa kiyayya a zukatan jama'a da kuma raba kawunan ‘yan kasar.
Tun a shekara ta 2001 aka kafa wannan kungiya, kuma ta ke gudanar da ayyukanta.
Tun a bara ne dai kasar Burundi ta fada cikin rudani sakamakon kankame wa madafun iko da shugaba Pierre Nkurunziza ya yi, in da ya nemi wa'adi na uku sabanin wa'adi biyu da kundin tsarin mulkin kasar ya tanadar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu