Isa ga babban shafi
najeriya

Majalisa ta amince da dokar kare masu tsegunta barayin gwamnati

Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da dokar da za ta kare mutanen da ke tsegunta wa hukumomi labarin aikata laifufukan da suka shafi cin hanci da rashawa a kasar.

Tambarin hukumar yaki da rashawa ta Najeriya
Tambarin hukumar yaki da rashawa ta Najeriya RFI / Pierre Moussart
Talla

Najeriya ta samar da wannan doka ne domin bai karfafa wa jama’a gwiwa ci gaba da bai wa hukumomin tsaro da kuma na yaki da rashawa irin wadannan labarai da ke bayar da damar gano wadanda ke yi wa tattalin arzikin kasar zagon kasa.

Shugaban kwamitin kula da ayyukan shari’a a majalisar dattawan Sanata David Umaru ya ce dokar za ta bai wa jama’a kariya domin sanar da mai unguwa, dagaci, sarakuna, jami’an ‘yan sanda ko kuma ofishin mai shigar da kara na gwamnati idan suna da labaran suka shafi cin hanci ko kuma handema dukiyar gwamnati a sassan kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.