Isa ga babban shafi
Najeriya

Bukukuwan sallah a mafi yawan kasashen duniya a wannan juma'a

A wannan juma’a musulmi a sassa da dama na duniya sun fara gudanar da bukukuwan babbar sallah ko kuma sallar layya, bayan da mahajjatan suka sauka daga hawan Arafa.

Raguna a birnin Dakar
Raguna a birnin Dakar AFP/Seyllou
Talla

A yammacin Afirka, kasashe kamar Najeriya, Benin, Mali da dai sauransu, ana bukukuwan babbar sallar ne a yau, yayin da a wasu kasashe irinsu Nijar da Senegal ke shirin gudanar da sallar a ranar asabar.

A sakon da ya aike wa al’ummar kasar dangane da zagayowar wannan rana, shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, bayan ya yi wa mahajjata fatan alheri, ya bukaci illahirin ‘yan kasar da su jingine bambancin da ke tsakaninsu domin samar da hadin-kai, wanda ya ce shi ne tushen samar da ci gaba ga kowace al’umma.

Ana gudanar da bukukuwan sallar ne bayan da mahajjata suka sauka daga hawan Arafa sannan suka fara aikin jifar Shaidan a Mina, kusa da Makka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.