Mahara sun kashe mutane 13 a Maiduguri
Wasu mata ‘yan kunar bakin wake su uku sun tarwatsa kansu tare da kashe mutane 13 sannan suka raunata wasu 16 a birnin Maiduguri da ke Najeriya.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Bayanai sun tabbatar da cewa da farko wata ‘yar kunar bakin wake ce ta tarwatsa kanta da misalin karfe 9 na daren lahadi a harabar wani gidan cin abinci, kafin daga bisani wasu ‘yan mata biyu su tayar da nasu bama-baman.
Duk da cewa ba wata kungiya da ta fito domin daukar nauyin kai hare-haren na daren jiya, to sai dai ana danganta lamarin da kungiyar Boko Haram da ta share tsawon shekaru tana aikata ayyukan ta’addanci a yankin arewa maso gabashin Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu