Isa ga babban shafi
Afrika

Shugabanin kasashen Afrika sun bukaci magance rikicin Togo

Shugabannin Kasashen Afirka sun bukaci shata hanyar magance rikicin siyasar kasar Togo domin kaucewa barkewar tashin hankali a fadin kasar.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da takwaransa na Cote 'D' Voire Alassane Ouattara yayin taron kungiyar tarayyar Turai da Afrika karo na 5 daya gudana a Ivory coast.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da takwaransa na Cote 'D' Voire Alassane Ouattara yayin taron kungiyar tarayyar Turai da Afrika karo na 5 daya gudana a Ivory coast. REUTERS/Luc Gnago
Talla

Shugabannin kasashen Najeriya da Cote d’Ivoire da Ghana da Burkinan Faso da Benin da kuma Guinea sun bukaci tattaunawa tsakanin wakilan Gwamnatin Togo da kuma Yan adawa ba tare da gindaya sharudodi ba.

Yan adawar Togo sun kwashe dogon lokaci suna gudanar da zanga zanga domin kawo karshen mulki shugaba Faure Gnassingbe wanda shi da mahaifin sa suka kwashe kusan shekaru 50 suna mulkin kasar.

Shugabannin na Afirka sun bayyana fargabar cewar rashin warware matsalar na iya haifar da rikicin da zai shafi Afirka ta Yamma baki daya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.