Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa za ta kasance mai shiga tsakani a rikicin Libya

A ranar talata mai kamawa ne Shugaban Faransa Emmanuel Macron zai ganawa da wasu magabatan Libya a Paris na kasar Faransa.

Shugaban Faransa da Firaministan Libya da Janar Haftar
Shugaban Faransa da Firaministan Libya da Janar Haftar REUTERS
Talla

Taron zai hada Firaministan kasar Fayez Al Sarraj, Janar Khalifa Haftar, Shugaban majalisar wakilan kasar Aguila Salah Issa da Shugaban kwamity zartarwa Khaled Al Mishri.

A wannan ganawa Shugaban Faransa na fatan samun hadin kan Shugabanin domin kawo karshen tankiyar da ake fuskanta tareda taimakawa don samar da gwamnati a kasar da zata samu goyan baya daga kasashen Duniya.

Shugaban Faransa ya gayato kasashen dake da hannu a rikicin Libya da sauren Shugabanin kasashe aminan Libya da za su iya taka gaggarumar rawa a zaman taron na Paris don kawo karshen rikicin kasar ga baki daya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.