Isa ga babban shafi

Shugaban Congo ya bukaci bai wa tsaffin shugabanni kariya

Majalisar Jamhuriyar Congo za ta yi zama na musamman akan kudurin da shugaban kasar Joseph Kabila ya mika mata, na samar da wata doka, da za ta bai wa shuwagabannin kasar kariya daga dukkan wata tuhumar aikata ba dai dai ba, bayan sauka daga mulki.

Shugaban Jamhuriyar Congo Joseph Kabila.
Shugaban Jamhuriyar Congo Joseph Kabila. REUTERS/Kenny Katombe
Talla

To sai dai har yanzu majalisar kasar ba ta yi karin bayani akan rana ko lokacin da za ta zauna domin muhawara akan wanna kuduri ba.

A karkashin dokar dai ba za a kama tsohon shugaba da mataimakansa ba, a dalilin aikata ba dai ba, zalika za a bai wa tsohon shugaban masu tsaron lafiyarsa na musamman, a kuma kara masa yawan kudaden fanshon da zai rika karba.

Wasu na kallon bukatar ta Kabila a matsayin alamar da ke nuni da cewa, shugaban ba zai sake neman tazarce ba, a zaben shugabancin kasar da zai gudana a watan Disamba mai zuwa, duk da cewa ‘yan adawa na zarginsa da shirya makarkashiyar kara wa’adinsa da ke gaf da karewa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.