Isa ga babban shafi
Najeriya

'Yan Boko Haram sun kashe mutane 9 a Najeriya

‘Yan Boko Haram sun kashe mutane 9 tare da raunata wasu 9 a harin baya bayan nan da suka kai cikin jihar Borno da ke tarayyar Najeriya.

Shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau
Shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau AFP PHOTO / BOKO HARAM
Talla

Wani mai suna Ibrahim Liman, jami’i a rundunar mayakan sa-kai da ake kira Kato da Gora, ya ce mayakan na Boko Haram sun kashe mutanen 9 ne a kauyukan Kalari Abdiye da kuma Amarwa wadanda ba su da nisa daga Maiduguri, yayin da suka raunata wasu mutane 9 na daban.

Lamarin ya faru ne a marecen jiya laraba, inda mayakan suka afka wa garin da misalin karfe 8 da rabi na dare lokacin da ake shatata ruwan sama.

Daga bisani mayakan na Boko Haram sun kona kauyukan biyu da ke cikin karamar hukumar mulkin Kondufga kurmus.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.