‘Yan sanda sun yi amfani da harsashi mai kisa kan masu zanga-zanga
Rahotanni daga Sudan sun ce ‘yan sandan kwantar da tarzoma sun yi amfani da harsashi mai kisa wajen kokarin tarwatsa daruruwan masu zanga-zanga, da ke kokarin isa fadar gwamnatin kasar a birnin Khartoum.
Wallafawa ranar:
Da fari dai jami’an tsaron sun yi amfani ne da hayaki mai sa hawaye wajen kokarin tarwatsa masu zanga-zangar, amma hakan bai samu ba, saboda sun ci gaba da tunkarar fadar gwamnatin ta hanyar amfani da kyallaye wajen rufe fuskokinsu.
Arrangamar tsakanin masu zanga-zanga da jami’an tsaro wadda ta auku a ranar Talata, ita ce mafi muni, tun bayan soma zanga-zanga da wasu dubban ‘yan kasar suka yi a sassa daban daban kan karin farashin biredi, wadda ta juye zuwa ta kin jinin gwamnati.
Hotunan bidiyo da aka wallafa a kafofin intanet, hadi da rahotanni sun nuna masu zanga-zangar na rera waken neman sauya gwamnati ta hanyar tilastawa shugaban kasar Omar al-Bashir ya yi murabus.
Sai dai yayin da yake yi wa wasu magoya bayansa jawabi a ranar ta Talata, shugaba al-Bashir ya zargi wasu ‘yan kasashen ketare da hannu wajen haddasa zanga-zangar, wadda ta zama mafi girma cikin shekaru da dama a tsawon lokacin da shugaba al-Bashir ya shafe yana mulkin Sudan na shekaru 29.
Alkalumman gwamnati sun ce mutane 12 suka mutu zuwa yanzu, sai dai a nata rahoton kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International ta ce masu zanga-zanga 37 ne suka mutu yayin arrangama da jami’an tsaro.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu